A duk lokutan da aka shafe inda
tattalin arzikin Zimbabwe ya yi ta tabarbarewa tsawon shekaru, an sha
hasashen durkushewar Robert Mugabe ta fuskar siyasa da ma ta lafiya, sai
dai ya tsallake wannan fata, har sai yanzu da wani abu ya faru.
Haka
kuma, ana ganin kamar ya wuce gona da iri wajen ganin cewa matarsa ta
gaje shi, hakan ne kuma ta sa shugabannin soji wadanda da bazarsu yake
rawa a mulkin, suka daina ba shi goyon baya.
Halin lafiyarsa dai
ya ci gaba da tabarbarewa cikin shekarun da suka gabata, kasancewar sa
dan shekara 93, duk da cewa a hukumance ya yi aniyar sake tsayawa
takara.
Kafin zaben shekarar 2008, ya ce: "Idan ka fadi zabe kuma mutane suka juya maka baya, to lokacin barin siyasa ya yi."
Amma
bayan da Morgan Tsvangirai ya yi nasara a kansa, sai Mista Mugabe ya
fiddo wasu halaye da suka saba da maganar tasa, inda ya yi rantsuwa cewa
'Allah ne kadai' zai iya tsige shi daga ofis.
Amma don ya tabbatar da ikon nasa, sai ya dinga amfani da rikici.
Shi
kuwa Mista Tsvangirai a kokarinsa na kare magoya bayansa, sai ya janye
daga zagaye na biyu, amma duk da haka an tilasta Mista Mugabe ya sanya
Mista Tsvangirai a matsayin mataimakinsa, shi kuma ya ci gaba da mulkin
da ya fara tun shekarar 1980.
Babban abun da ya sa Mista Mugabe ya yi suna shi ne yakin da aka yi a shekarun 1970. Tarihin rayuwar Robert Mugabe
Image caption
Shugaba Mugabe ya bai wa matarsa Grace goyon bayan zama mataimakiyar shugaba
1924: Shekarar da aka haife shi
An horar da shi a matsayin malami
1964: Gwamnatin Rhodesia ta daure shi
1980: Ya lashe zaben da aka yi bayan 'yancin kai
1996: Ya auri Grace Marufu
2000: Bai yi nasara ba a zaben raba-gardamr da aka yi ba na karfin ikon shugaban kasa da kuma hana Turawa mallakar gonaki
2008: Ya zo na biyu a zagayen farko na zaben da suka fafata da Tsvangirai, wanda ya janye saboda harin da aka kai kan magoya bayansa
2009: Ya rantsar da Tsvangirai a matsayin firai minista a lokacin da ake fuskantar durkushewar tattalin arziki a kasar
2016: An gabatar da takardun lamuni a yayin da karancin takardun kudya yi tsanani
2017: Ya kori mataimakinsa da ya dade suna aiki tare wato Emmerson Mnangagwa
Jigo a juyin-juya hali
Akwai
lokacin da ake yi masa kallon wani jigo a juyin-juya hali, inda yake
fada da tsirarun Turawa don neman 'yancin al'ummarsa - wannan ne dalilin
da ya sa shugabannin Afirka da dama suke sako-sako wajen sukar sa.
Tun bayan da Zimbabwe ta samu 'yancin kai, an samu ci gaba a duniya, amma shi har yanzu tunaninsa na zamanin da ne.
Image caption
Ana iya ganin Robert Mugabe nan (a hagu), cikin
1960, inda ya samu kaimi daga akidojin naka-sai-naka a Afirka
Har yanzu jaruman yakin kwato yanci na jam'iyyar Zanu-PF na yakar munanan akidun jari hujja da mulkin mallaka.
A
kan yi watsi da masu suka ana kwatanta su da maciya amana, abin da ke
tunowa da yakin sari-ka-noke, lokacin da alakanta mutum da wannan kalmar
tamkar hukuncin kisa ne.
Ya sha dora alhakin matsin tattalin
arzikin da Zimbabwe ke fama da shi a kan kasashen yamma, karkashin
jagorancin Birtaniya, don hambarar da shi saboda kwace gonakin Turawa da
ya yi.
Masu sukarsa na yawan zargin sa da cewa ba ya nuna damuwa kan yadda tattalin arzikin zamani ke aiki.
Ya fi mayar da hankali kan tambayar yadda za a raba zarikin kasa, maimakon neman hanyar da za a inganta shi.
Image caption
Masu zanga-zanga a shekarar 2016 sun kona kudin
kasar da ba shi da daraja don nuna kin amincewa da gabatar da takardun
lamuni a matsayin kudi
Mr Mugabe ya taba cewa tattalin arzikin kasar da zai
taba durkushewa gaba daya ba, kasancewar kasarsa ta fuskanci matsalar
tattalin arziki mafi kamari a duniya, da kuma hauhuawar farashi da ya
taba kai wa kashi miliyan 231 a watan Yulin 2008, kai ka ce yana so ne
ya gwada ikirarin nasa.
Farfesa Tony Hawkins na jami'ar Zimbabwe
ya taba fuskantar wani abu tattare da shugaban Zimbabwe, inda ya ce: "A
duk lokacin da batun tattalin arziki ya hadu da siyasa, to siyasa ce ke
yin nasara."
A shekarar 2000, ya fuskanci kakkarfar hamayya a
karon farko, ya damalmala tattalin arzikin kasar don samun karfin iko a
siyance.
Ya kwace gonakin Turawa wadanda su ne kashin bayan
tattalin azrikin kasar, ya kuma fatattaki kungiyoyin tallafi, wato dai
cikin siyasa Mista Mugabe ya yi wa makiyansa shigar-burtu - ya ci gaba
da kasancew a mulki.
Ko ta halin kaka
Kuma dabarun da shi da magoya bayansa suka yi amfani da su, sun samo su ne daga yakin sari-ka-noken da aka yi a can baya.
Bayan
da ya sha kaye a karon farko a zaben raba gardamar shekarar 2000, Mista
Mugabe ya kaddamar da mayakan sa kai na kashin kansa, wasu tsofaffin
sojoji 'yan mazan jiya, da dakarun tsaro ke marawa baya - wadanda ke
amfani da rikici da kashe-kashe a matsayin matakan zabe.
Image caption
Mista Mugabe na cewa yana gwagwarmaya ne don kwatar 'yancin bakaken fata 'yan Zimbabwe
Bayan shekara takwas, an sake bin irin wannan salon bayan da Mista Mugabe ya fadi a zagayen farko na zaben shugaban kasa.
A
duk lokacin da aka bukata, a kan yi amfani da dakarun tsaro da kafafen
yada labarai na gwamnati, wadanda mambobin jam'iyyar Zanu-PF ne, wajen
yi wa jam'iyya mai mulki hidima.
Mutumin wanda ya yi gwagwarmaya
kan mutum-daya, kuri'a-daya ya bullo da wani sharadi na cewa mutanen da
suka cancanci zabe sai sun tabbatar sun 'yan kasa ne ta hanyar gabatar
da takardun shaida na biyan kudin lantarki ko ruwan famfo, abin da kyar
ne matasa da tsantsar masu zabe marasa aikin yi 'yan adawa, idan suna da
su.
Daya daga cikin nasarorin da tsohon malamin da ya shafe
tsawon shekara 33 a kan mulki, ba ko tantama ya iya cimmawa ita ce
fadada ilmi.
Zimbabwe a baya-bayan nan na da alkaluman mutanen da suka iya karatu da rubutu mai yawa a Afirka da kashi 90% na al'ummarta.
Masanin
kimiyyar siyasa a yanzu marigayi Masipula Sithole ya taba cewa bunkasa
ilmin da shugaban kasar ke yi tamkar "hakawa kansa kabari" ne.
Matasan
da suka ci gajiyar haka na iya yin tankade da rairaya kan matsalolin
Zimbabwe da kansu kuma akasari suna zargin cin hanci da rashin iya
gudanarwar da suka dabaibaye gwamnati a matsayin silar rashin samun
ayyuka da kuma hauhawar farashi.
Mai riƙon ƙaho
Mista
Mugabe na iya yin imani cewa abu ne mai sauki a mulki kasar manoma masu
neman abin da za su kai cikinsu da saurin mika wuya a kan zaratan
matasa masu karfi a jika da suka koshi da ilmi.
Ya yi ikirarin yana gwagwarma ne don talakawan karkara sai dai filaye da dama da ya kwace sun koma hannuwan 'yan barandansa.
Mugabe bai taba tsoron yin amfani da tarzoma ba don ci gaba da mulki
Babban limamin kiristan nan, Desmond Tutu ya taba
cewa dadadden shugaban na Zimbabwe ya zama kwatankwacin 'yan kama-karyan
Afirka masu riƙon ƙaho.
A lokacin gangamin yakin neman zaben
shugaban kasa na 2002, ya fara sanya riguna masu launukan sheki da ke
dallare fuskarsa - wani salo na shugabannin Afirka masu mulkin danniya.
A
cikin shekaru ashirin dinsa na farko, ana ganin dan ra'ayin riƙwan ne
kawai a bainar jama'a cikin shigar jaket da lakatayel ko kuma hartin da
wando.
An bar 'yan Zimbabwe da yawa, har ma da wasu na tambayar
me ya sa ba zai sawwake wa kansa ya je ya huta a 'yan shekarun da suka
rage masa da matashiyar matarsa ba.
Matarsa ta biyu, Grace, wadda ya ba wa ratar shekara
40, ta taba cewa yakan tashi da karfe hudun dare ya kama motsa jikin da
ya saba kullum.
Mista Mugabe yana dan shekara 73 lokacin da ta haifa musu dansu na uku, Chatunga.
Yana
da'awar shi riƙaƙƙen dan katolika ne, kuma lokaci-lokaci jami'an tsaro
kan mamaye masu ibada a Majami'ar Katolika ta Harare duk ranar Lahadin
da ya je addu'a.
Sai dai, imanin Mugabe bai hana shi samun 'ya'ya
guda biyu da Grace ba, lokacin da take sakatariyarsa, yayin da
fitacciyar uwargidansa mutuniyar Ghana, Sally, ke fama da jinyar ajali
sakamakon cutar kansa. 'Sarki'
Ko
da yake, Robert Mugabe ya yi wa mutuwar da ake ta kira masa ƙwari, sai
dai shekarun da suka laftu a kansa sun fara yi masa nauyi a baya-bayan
nan, inda kaifin bakin da aka san shi da shi a baya, yanzu kan koma cike
da gajiya idan yana jawabi.
Wani sakon diflomasiyya na Amurka a
shekara ta 2011, da shafin kwarmata bayanai na Wkileaks ya fitar na nuna
cewa Mugabe na fama da cutar daji.
Image caption
Matarsa Grace ta ce Mista Mugabe kan farka tsakar dare don motsa jininsa
Idan ba wannan ba, a ko da yaushe Mista Mugabe ya kasance mutum mai tsananin alfahari.
Sau da dama yana cewa zai sauka daga mulki ne kawai idan kammala cika burinsa na "juyin juya hali".
Wannan
na nufin sake raba gonakin fararen fata, yana kuma so ya zabi mutumin
da zai gaje shi da hannunsa, wanda tabbas zai fito daga cikin
jam'iyyarsa ta Zanu-PF.
Didymus Mutasa, da ya taba zama
makusantan Mista Mugabe amma yanzu sun yi hannun riga, ya taba fada wa
BBC cewa a al'adar Zimbabwe, ana maye gurbin sarakuna ne kadai idan sun
mutu "kuma Mugabe sarkinmu ne".
Sai dai ga alama kamar wasu daga cikin tsoffin abokan tafiyarsa ba su shirya wa kafuwar daular ba.