Labari mai dadi: Gwamnatin Najeriya ta biya sojoji dake yakar Boko Haram kudin watanni biyu da suke bi

Daga
karshe ma’aikatar tsaro ta saki kudade don biyan alawus na rundunar sojin Najeriya dake yaki da yan ta’addan Boko Haram a Arewa maso gabas da kuma wadanda ke gudanar da ayyuka daban daban a fadin kasar.
A wata sanarwa da ya saki a ranar Litinin, kakakin rundunar soji, Birgediya Janar Sani Usman yace shugaban hafsan soji Tukur Buratai yayi umurni gas akin kudin a ranar Litinin.
A ranar Lahadi ne, Buratai ya aika wani sako na musamman don bayar da tabbaci da kuma karfafa ma sojoji gwiwa a aiki da suke a gida da wajen kasar.
Hakan ya biyo bayan korafi da sojoji dake yakar ta’addanci a arewa maso gabas suka yi kan cewa basu samu alawus dinsu na tsawon watanni biyu ba.

Labels: